fidelitybank

Zuwa kotu ɓata lokaci ne – Dan takarar gwamnan SDP a Kogi

Date:

Ɗan takarar jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) a zaɓen gwamnan jihar Kogi ya yi zargin cewa an yi maguɗi a zaɓen na ranar Asabar, yana mai cewa ba zai je kotu ba “saboda ɓata lokaci ne”.

Murtala Ajaka wanda ya zo na biyu a sakamakon da hukumar zaɓe Inec ta bayyana, ya faɗa wa kafar talabijin ta Channels TV cewa zuwa kotu ɓata lokaci ne “saboda hukumar zaɓen za ta je kotun kuma ta kare sakamakon da ta bayyana”.

Inec ta ce Usman Ododo na jam’iyyar APC ne ya yi nasara bayan ya samu ƙuri’a 446,237, sai Ajaka da ya samu 259,052, da kuma Dino Melaye na PDP mai ƙuri’a 46,362.

“Na shafe shekara 20 ina siyasa, saboda haka na san yadda lamarin yake. Me zan je kotu na yi bayan Inec ɗin da suka yi wannan abin za su je kotun a matsayin waɗanda ake ƙara kuma su kare abin da suka aikata?” in ji Ajaka.

“Wannan ɓata lokaci ne kawai, sai dai jam’iyya [ta kai ƙara] amma ni kam raina ya ɓaci sosai.”

Tun kafin a kammala tattara sakamakon zaɓen, ɗan takarar PDP Sanata Dino Melaye ya yi watsi da shi, yana mai neman Inec ta soke shi gaba ɗaya.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp