Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Muna Elbadawy da ya kama da gobara a jihar.
Zulum ya umarci hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Borno (SEMA) da ta lissafa tare da mika bayanai kan adadin gidajen da gobara ya shafa ,domin gwamnatin jihar ta tallafa musu.
Zulum ya kai ziyarar ne a ranar Asabar, 19 ga watan Fabrairu, inda ya zagaya wajen da annobar ta afku.
Gobarar wacce ta tashi a sansanin ‘yan gudun hijirar da ke wajen Maiduguri, ta hallaka rai daya, sannan ta jikkata mutane 17, yayin da ta lalata matsuguni sama da guda 100.
Sansanin na dauke da gidaje fiye da 10,000 da mutane 50,000 ke zaune.
Gwamnan ya kuma sanar da cewar, gwamnatin jihar na duba yiwuwar hada hannu da gwamnatin tarayya da hukumomin agaji, domin mayar da su da sauran ‘yan gudun hijira da ke Maiduguri da kewaye, zuwa gidajensu ko garuruwa mafi kusa irin su Ngwom da sauransu.