fidelitybank

Zulum ya ware gidaje 259 da Naira miliyan 110 ga ƴan sanda

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, a ranar Alhamis a Maiduguri, ya bayyana cewa, gwamnati ta ware gidaje 259 tare da sakin Naira miliyan 110 ga rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar.

Zulum ya bayyana hakan ne a lokacin kaddamar da bankin ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Borno (NPFM Bank).

An tsara bankin Microfinance ne don samar da ayyukan kudi don tallafa wa kanana da matsakaitan sana’o’i ga iyalan ‘yan sanda, ‘yan uwansu da fararen hula a jihar Borno.

Bude bankin a Maiduguri ya samu halartar babban sufeton ‘yan sanda, Usman Baba Alkali.

Na farko, in ji Zulum, an yi amfani da Naira miliyan 25 don raba wa iyalan ‘yan sandan da suka mutu a bakin aiki.

Ya ba da umarnin a ajiye kudaden a asusun ajiyar yaran da jami’an ‘yan sandan da suka mutu suka bari a baya.

Kudaden Naira miliyan 30, inji gwamnan, za a saka shi a asusun ajiyar kudi, domin tallafa wa matan ‘yan sanda da ke aiki a fadin jihar Borno.

Zulum ya yabawa IGP Alkali, bisa kaddamar da reshen bankin na Borno wanda ya ce, ya nuna yadda IGP ya ba da fifiko ga jin dadin ‘yan sanda.

assu today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp