fidelitybank

Zulum ya umarci da a duba mutanen da ‘yan Boko Haram suka jikkata kyauta

Date:

Mutum takwas sun sun mutu yayin da wasu da dama suka jikkata bayan da wata motar bas ta taka nakiya a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa a ranar Asabar.

Gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya zargi ƙungiyar Boko Haram da dasa nakiyar a kan babban titi da ya haɗa Maiduguri, babban birnin jihar da kuma garin Damboa.

A baya rundunar sojin Najeriya ta rufe titin sakamakon ta’azzarar matsalolin tsaro a yankin.

Daga baya ne gwamnan jihar ya bayar da umarnin buɗe titin inda sojoji ke bai wa matafiya kariya ta hanyar yi musu rakiya.

To sai dai gwamnan ya ce harin na jiya Asabar ba zai sa a daina bin titin ba.

“Za mu tabbatar da cewa an ci gaba da zirga-zirga tsakanin Maiduguri zuwa Damboa, wannan hari ba zai hana mu bin titin ba,” in ji Gwamna Zulum.

Dasa nakiyoyi ya kasance ɗaya daga cikin hanyoyin da ƙungiyar Boko Haram ke kai hare-hare. Ko a shekarar da ga gabata ma irin wannan hari ya kashe sojojin ƙasar bakwai, bayan da motarsu ta taka nakiya.

A baya-bayan nan dai hare-haren Boko Haram na sake dawowa musamman a jihar Borno, lamarin da ya sa gwamnan jihar ya fito ya koka a baya-bayan nan.

guardian newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp