Mutum takwas sun sun mutu yayin da wasu da dama suka jikkata bayan da wata motar bas ta taka nakiya a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa a ranar Asabar.
Gwamnan jihar Babagana Umara Zulum ya zargi ƙungiyar Boko Haram da dasa nakiyar a kan babban titi da ya haɗa Maiduguri, babban birnin jihar da kuma garin Damboa.
A baya rundunar sojin Najeriya ta rufe titin sakamakon ta’azzarar matsalolin tsaro a yankin.
Daga baya ne gwamnan jihar ya bayar da umarnin buɗe titin inda sojoji ke bai wa matafiya kariya ta hanyar yi musu rakiya.
To sai dai gwamnan ya ce harin na jiya Asabar ba zai sa a daina bin titin ba.
“Za mu tabbatar da cewa an ci gaba da zirga-zirga tsakanin Maiduguri zuwa Damboa, wannan hari ba zai hana mu bin titin ba,” in ji Gwamna Zulum.
Dasa nakiyoyi ya kasance ɗaya daga cikin hanyoyin da ƙungiyar Boko Haram ke kai hare-hare. Ko a shekarar da ga gabata ma irin wannan hari ya kashe sojojin ƙasar bakwai, bayan da motarsu ta taka nakiya.
A baya-bayan nan dai hare-haren Boko Haram na sake dawowa musamman a jihar Borno, lamarin da ya sa gwamnan jihar ya fito ya koka a baya-bayan nan.