Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya raba tireloli 10 na kayan abinci da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya ba jihar gudunmuwa.
Gwamna ya ƙaddamar da rabon ne a ranar Litinin a wasu cibiyoyi ga mazauna Gambarou da Ngala da sauran garuruwa, inda aka samu tsaikon abinci a sanadiyar ambaliyar ruwa da ta ɗaiɗaita babban birnin jihar.
Kayan hatsin sun ƙunshi masara da gero da dawa, kuma an raba ga iyalai ne, musamman ga waɗanda suka fi fama da rashin abinci.
Da yake yi wa manema labarai jawabi bayan ƙaddamar da raba abincin, Zulum ya ce an zaɓi Ngala ne, “saboda sai da ambaliyar ta raba garin baki ɗaya daga sauran ɓangarorin jihar na kusan wata huɗu. Wannan ya sa muko zo nan a yau domin ƙaddamar da rabon abincin nan domin rage wa mutanen yankin raɗaɗin da suka shiga.”
Zulum ya yaba wa shugaban ƙasa Bola Tinubu da sauran hukumomin gwamnatin tarayya bisa goyon bayan da suka ba jihar.
“Dukkan abinci da muka raba a yau, shugaban ƙasa Bola Tinubu ne ya ba mu. Muna godiya ga gwamnatin tarayya bisa wannan goyon baya.