fidelitybank

Zulum ya raba kayan abinci ga marasa karfi a Borno

Date:

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya sanya ido kan shirin rage raɗaɗi da ya ƙunshi tallafin abinci ga iyalai 2,000 a mazaɓar Mafoni da ke birnin Maiduguri.

Wata sanarwa da Mallam Isa Gusau mai magana da yawun gwamnan ya fitar ta ce manufar rabon abincin ita ce rage raɗaɗin cire tallafin man fetur, kuma yayin rabon an bai wa kowanne gida buhun shinkafa da wake biyu.

Zulum ya bayyana cewa an zaɓo waɗanda suka ci gajiyar shirin ne daga mazaɓa 27 daga faɗin Maiduguri da kuma mazaɓa 12 daga ƙaramar hukumar Jere.

Sanarwar ta ce rabon abinci wanda ya ƙunshi buhun shinkafa 54,000 da buhunnan wake 54,000, an bayar ne ga magidantan da suka fi buƙata a cikin ƙananan hukumomin jihar biyu, a cewar gwamnatin.

Ta ƙara da cewa gwamnatin Zulum ta tashi haiƙan wajen neman dabarun da za su rage illar da hauhawar farashin man fetur ta haifar a kan talakawa, ta hanyar tabbatar da ganin abinci da sauran muhimman ayyuka ga masu tsananin buƙata.

Da yake jawabi a wurin raba abincin, Gwamna Zulum ya ce buhunnan shinkafar wani ɓangare ne na shinkafa buhu 3,000 da gwamnatin Borno ta karɓa daga Shugaba Bola Tinubu.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp