Gwamnan JIhar Borno Farfesa Babagana Zulum, ya karɓi ƙarin gudun hijira 855 karo na biyu, waɗanda Kamaru dake makwaɓtaka ta maida musu.
An miƙa wa Zulum waɗannan ‘yan cirani da hukumomin Kamaru suka dawo da su, wanda gwamnan Arewa mai nisa Minjinyawa Bakari,ya jagoranci maƙawa a Marouwa a ranar Talata.
Lokacin da yake yi musu bankwana tare da miƙa musu kyautar abinci da wasu kayan, Bakari ya sanar da cewa sun mayarwa da Najeriya ‘yan gudun hijira 1,300 cif-cif.
A madadin Najeriya Zulum ya karbi waɗannan ‘yan gudun hijira ya godewa shugaban Kamaru, tare da sauran masu ruwa da tsaki da suka riƙe waɗannan mutane kimanin shekara 9 a hannunsu.
Ka zalika ya yi wa Shugaba Paul Biya godiya na kyautukan da ya rabawa mutanen.