Gwamnan Jihar Borno Umara Baba Gana Zulum, ya bayar da umarnin kafa bankunan al’umma da za su yi aikin sauyawa al’ummar jihar tsofaffin kuɗaɗensu a duka jihohi 27 da Jihar take da su.
Umarnin na Gwamna Zulum na zuwa ne bayan umarnin da CBN ya yi na a dakatar da karɓar tsofaffin takardun kuɗi a karar nan da 31 ga watan Janairun da muke ciki, umarnin ya shafi duka ƙanann hukumomin jihar 25 cikin 27 da take dasu, wadanda rikicin Boko Haram na tsawon shekara 12 ya shafa.
Gwamnan ya sanar da ɗaukar wannan mataki ne a Maiduguri a ranar Laraba, yayin wata tattaunawa ta masu ruwa da tsaki wadda Shehun Borno Abubakar Umar Garbai Elkanemi ya halarta, wanda Wazirin Borno ya wakilta.
Tuni aka yanke shawarar za a fara aiwatar da umarnin a ƙanan Monguno da Gwoza.