fidelitybank

Zulum ya bayar da umarni a sake gyara asibitin kwararru na Borno

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, a ranar Asabar ya bayar da umarnin sake gyara asibitin kwararru na jihar da ke Maiduguri, tare da gina sabbin gine-gine.

Zulum ya kuma ba da umarnin gyara gidan Buba Marwa, wanda ke zama wurin kwana ga likitocin da ke aiki a asibitin kwararru.

Gwamnan ya ba da umarnin biyu a ranar Asabar da yamma yayin ziyarar tantancewar da ya kai asibitin.

“Mun yi nazarin karfin asibitin, kuma nan ba da jimawa ba za mu fara gina wasu gine-gine tare da yin wasu gyare-gyare ta yadda likitoci da sauran ma’aikatan lafiya za su samu ofisoshi a harabar,” in ji Zulum.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa za a sayo kayan aikin jinya tare da daukar karin ma’aikatan jinya da suka hada da likitoci da ma’aikatan jinya.

“Gwamnatin jihar Borno za ta sayo kayan aikin jinya da ba a samu a asibiti a halin yanzu. Za mu dauki karin likitoci da ma’aikatan jinya tare da tabbatar da cewa an samar da wuraren wanki,” in ji Zulum.

Ya kara da cewa, “dukkan wadannan yunƙurin an yi niyya ne don sake saita tsarin kiwon lafiya a jihar Borno.”

Gwamna Zulum ya samu rakiyar sakataren gwamnatin jihar Bukar Tijjani da wasu manyan jami’an gwamnati.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp