fidelitybank

Zulum ya baiwa Sojojin da suka jikkata tallafin Naira miliyan 10

Date:

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum, ya bayar da tallafin naira miliyan 10 ga sojojin da suka jikkata sakamakon yaƙi da Boko Haram da suke yi a jihar.

Cikin wani saƙo da gwamnan ya wallafa shafinsa na X da a baya aka fi sani da Twitter, ya ce tallafin na daga cikin alƙawarin da ya ɗauka, wata biyu da suka gabata a lokacin da babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya kai ziyara jihar.

Babban hafsan sojin ƙasan dai ya je jihar ne domin gudanar da bukukuwan babbar sallar tare da dakarun ƙasar da ke fagen daga a jihar ta Bornon.

Kwamishinan yaɗa labarai da tsaron cikin gida Farfesa Usman A Tar tare da babban sakataren gidan gwamnatin jihar Barrister Mustapha Ali Busuguma ne suka miƙa kuɗin ga babban kwamandan runduna ta bakwai da ke Maiduguri, Manjo Janar Peter Malla ranar Asabar.

Sojojin Najeriya da dama ne suka mutu a rikicin Boko Haram da aka ƙwashe fiye da shekara 10 ana yi a yankin arewa maso gabashin Najeriya, musamman jihohin Borno da Yobe da wasu yankunan jihar Adamawa.

Lamarin da yayin sanadiyyar mutuwar dubban fararen hula da raba miliyoyi da muhallansu.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp