fidelitybank

Zulum ya ɗage dokar hana zirga-zirga a Borno

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ɗage dokar taƙaita zirga-zirga da aka sanya a jihar, bayan fashewar bom a Kawori ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 16 tare da jikkata wasu.

Yayin da yake jawabi da aka yaɗa a kafofin yaɗa labaran jihar, Gwamna Zulum ya jajanta wa iyalan waɗanda suka mutu a harin na Kawori.

”Ina miƙa saƙon ta’aziyyar ga iyalan waɗanda harin ya shafa da kuma duka mutanen Borno, ina kuma jajanta wa waɗanda suka jikkata, waɗanda a yanzu haka ke asibiti suke kuma samun kulawar likitoci”.

Gwamnan ya kuma ce tun da farko an sanya dokar ne domin hana mayaƙan Boko Haram amfani da damar wajen haifar da tashin hankali a jihar.

Ya ƙara da cewa ɓata-gari ne suka yi shigar burta domin shiga cikin masu zanga-zangar lumana, inda suka yi yunƙurin kawo hargitsi, sai dai a cewarsa jami’an tsaro sun samu nasarar kwantar da hankula.

Yayin da yake bayyana janye dokar taƙaita zirga-zirgar, Gwamna Zulum ya ce mutane su fita harkokinsu, amma jami’an tsaro za su ci gaba da sanya idanu, domin magance duk wani abu da suka ga zai kawo tashin hankali.

vanguardnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...
X whatsapp