fidelitybank

Zimbabwe ta nemi tallafin Sojin Najeriya

Date:

Babban kwamandan sojin sama na Zimbabwe, Air Marshal Elson Moyo, ya bayyana buƙatar ƙasarsa na neman tallafin dabarun aiki daga rundunar sojin saman Najeriya.

Moyo ya bayyana buƙatar ne a lokacin da ya ziyarci babban hafsan sojin saman Najeriya Air Marshal Oladayo Amao, a shalkwatar rundunar sojin saman Najeriya da ke Abuja babban birnin ƙasar.

Daraktan sashen hulda da jama’a da yaɗa labarai na rundunar Air Commodore Ayodele Famuyiwa, ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.

Babban kwamandan sojin saman Zimbabwe ya buƙaci tallafin rundunar sojin saman Najeriyar a ɓangarorin da suka shafi bincike da ci gaba, da fannin fasahar jiragen yaƙi da gudanarwa da yadda za a yi aiki da jiragen yaƙin ƙirar F7 da Mi-35.

Moyo ya ce ɓangarorin da ƙasarsa ke neman taimakon Najeriyar, ɓangarori ne da rundunonin sojin saman ƙasashen biyu duka ke amfani da su, musamman jiragen yaƙin da ƙasashen biyu ke amfani da su.

Ya ce a cikin ɗan takaitaccen lokaci rundunar sojin saman Najeriya ta samu gagarumin ci gaba wajen gina kanta da amfani da dabarun cikin gida.

A yayin da yake jawabi a nasa ɓangaren, babban hafsan sojin sama na Najeriya Air Marshal Oladayo Amao, ya ce rundunar a shirye take domin ƙulla ƙawancen da zai amfanar da juna tsakaninta da takwararta ta Zimbabwe.

Amao ya ce, a yanzu haka rundunar sojin saman Najeriya ta ƙulla ƙawance da ƙasashe da dama a nahiyar Afirka da ma wajenta, yana mai cewa a kodayaUshe rundunar a shirye take domin taimaka wa ƙasashen da ke buƙatar taimakonta.

Ya ƙara da cewa haɗin kai tsakanin rundunonin sojin ƙasashen Afirka zai taimaka wajen magance matsalolin tsaron da nahiyar ke fuskanta

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp