fidelitybank

Zimbabwe ta amince da kudirin hana hukuncin kisa

Date:

Gwamnatin Zimbabwe ta amince da wani kudirin doka da zai soke hukuncin kisa a ƙasar.

Matakin na zuwa ne kusan shekaru 20 bayan da kasar ta aiwatar da hukuncin kisa na karshe.

Majalisar zartaswar ƙasar dai ta goyi bayan kudurin dokar da za ta kawo ƙarshen hukuncin kisa.

Ministan yaɗa labaran kasar Jenfan Muswere a ranar Talata ya ce majalisar ministocin ta yanke shawarar ne bayan da gwamnatin ƙasar ta amince da kudirin doka.

Majalisar ministocin kasar Ta ba da shawarar maye gurbin hukuncin kisa da daurin rai da rai a matsayin mafi girman hukunci a ƙasar. A cewar BBC.

A baya dai, shugaban ƙasar, Emmerson Mnangagwa ya soki hukuncin kisa.

An taɓa yanke masa hukuncin kisa a shekara ta 1965 bayan zargin da aka yi masa na tayar da bam a cikin jirgin kasa a lokacin da yake yaƙi da ‘yan tsiraru fararen fata.

Sai daga baya kuma aka sassauta hukuncin kisan na Mista Mnangagwa bayan lauyoyinsa sun yi zargin cewa bai kai shekaru ba, bisa doka, maza masu shekaru tsakanin 21-70 ne kawai za a iya kashe su.

Hukuncin kisa na Zimbabwe ragowa ne na dokar zamanin mulkin mallaka. Tun shekarar 2005, ƙasar ba ta aiwatar da hukuncin kisa ba.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp