Yayin da Najeriya ke shirin gudanar da zaben shugaban kasa, wasu masu zanga-zanga sun yi dafifi a gaban ofishin tsohon shugaban kasar Goodluck Jonathan a Abuja suna neman ya sake tsayawa takarar mukamin shugaban kasar a zaben shekarar 2023.
Mutanen wadanda suka ce ‘ya’yan wata kungiya ce ta matasa, sun isa ofishin ne dauke da sakonni bisa takardu da ke kira ga tsohon shugaban ya fito ya tsaya takara.
Wasu takardun na dauke da hotunan Mista Jonathan inda suke cewa: “Sai ka tsaya takara Goodluck Jonathan. Muna bukatar ka ceto Najeriya”.
Kakakin kungiyar, Mayor Samuel, wanda shi ne mai kungiyar Youth Compatriots of Nigeria ya ce, “Wadanda suka ce a mika musu mulki a 2015, cewa za su gyara kasarmu sun yaudare mu”.