Gwamnonin jam’iyyar PDP a ranar Litinin sun gana da tsohon shugaban kasa na mulkin soja Ibrahim Babangida a garin Minna na jihar Neja.
Gwamnonin da suka halarci taron sun hada da Nyesom Wike na jihar Rivers, Seyi Makinde na jihar Oyo, Ifeanyi Ugwuanyi na jihar Enugu da Okezie Ikpeazu na jihar Abia.
Sauran manyan baki da suka halarci taron sun hada da tsohon shugaban kasa Janar Abdulsalami Abubakar, Sanata Gabriel Suswam, Sanata Sulaiman Nazif da Sanata Olaka Nwogu.
Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala taron, mataimakin shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Ikpeazu, ya ce, tawagar ta je Minna ne domin tuntubar tsohon shugaban kasa kan tunkarar zaben 2023.
“Na zo da takwarorina, Gwamnan Rivers, Gwamnan Enugu, Gwamnan Oyo, da wasu ‘yan Majalisar Dokoki ta kasa da sauran masu ruwa da tsaki,” inji shi.
“Na farko, tuntubar tsohon shugaban kasa, mu tattauna batutuwan da suka shafi kasa: ci gaban tattalin arziki, tsaro, da hadin kan kasarmu.