fidelitybank

Zaɓen 2023: EFCC ta tura jami’ai 200 a Kano da Jigawa da Katsina

Date:

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) a ranar Juma’a ta ce, ta tura jami’an tsaro dari biyu da ke yaki da sayen kuri’u a jihohin Kano, Jigawa da Katsina a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a yi ranar Asabar.

Kwamandan hukumar EFCC na shiyyar Kano Farouk Dogondaji ne ya bayyana haka yayin wata tattaunawa da NAN a Kano.

Dogondaji ya ce tura sojojin wani bangare ne na kudirin EFCC na tabbatar da sahihin zabe na 2023 a shiyyar.

Ya ce, “Mun tura jami’ai 50 domin sanya ido kan yadda zaben ke gudana a jihar Kano, hamsin a jihar Jigawa, hamsin kuma a jihar Katsina domin hana sayen kuri’u a duk lokacin gudanar da zabe.

“Sauran jami’ai [hamsin] an tura su zuwa filin jirgin saman Malam Aminu Kano da ke Kano da kuma filin jirgin Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina.”

A cewar Dogondaji, hukumar na da isassun jami’an tsaro, inda ya kara da cewa a shirye suke don fuskantar duk wata barazana ko da a lokacin zabe da kuma bayan zaben.

A yau Asabar ne za a gudanar da babban zaben shekarar 2023 a fadin Jihohin Najeriya 36 ciki har da babban birnin tarayya.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp