Zazzabin Lassa ta lashe rayukan mutane uku a jihar Benue daga cikinsu akwai wani likita mai suna, Samuel Nytyo, wanda ma’aikacin hukumar lafiya ta duniya (WHO) ne a jihar.
Sai dai kwamishinan lafiya na jihar, Joseph Nbgea ya bayyana cewa asibitin ya samu labarin mutuwar mutum daya, Dr. Nytyo wanda ya rasa ransa, sakamakon cutar a ranar Lahadin da ta gabata.
Majiya mai zaman kanta ta Daily Independent daga Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Benue (BSUTH) ta sake nanata cewa, wasu mutane biyu, baya ga likitan kuma sun mutu, sakamakon zazzabin Lassa.
Likitan da ya yi rashin lafiya a Benuwai an kai shi asibitin kwararru na Irrua, jihar Edo inda ya rasu, yayin da sauran biyun suka rasu a makon jiya.