Cibiyar da ke daƙile cutuka masu yaɗuwa ta Najeriya, NCDC ta ce ta samu mtum 3,465 da ake zaton zazzaɓin Lassa ne ya kama su inda aka tabbatar da mutum 645 da suka kamu da cutar sannan kuma mutum 118 suka rasu a tsakanin watan Janairu da na Maris ɗin 2025.
Cibiyar ta faɗi hakan ne a ranar Lahadi inda ta ƙara da cewa ɓarkewar cutar ya shafi ƙananan hukumomi 91 na jihohi 33 na ƙasar.
Darekta Janar na cibiyar, Dr Jide Idris ya bayyana cewa ma’aikatan lafiya 20 sun kamu da cutar a jihohin da suka haɗa da Ondo da Bauchi da Edo da Taraba da Ebonyi da Gombe da Benue da Ogun.