A yammacin ranar Litinin ne wani mutum da ba a san ko wanene ba, wutar lantarki ta kashe shi a lokacin da ya yi yunkurin lalata na’urar taransifoma a Osogbo.
Mutumin, a cewar majiyoyin al’umma, ya mutu ne a lokacin da kwatsam aka dawo da wutar lantarki a na’urar taransfoma, a lokacin da yake yunkurin sace na’urar lantarki.
Jaridar DAILY POST ta ruwaito cewa taransfomar tana nan ne a unguwar Kolade Estate, unguwar Onward, Ogo-Oluwa, Osogbo.
Rahotanni sun kuma bayyana cewa hukumar da ta dace ta dauke gawar mutumin