fidelitybank

Zargin ƙazafi: Gwamna Masari ya nemi ƴan jaridar Abuja su biya shi diyyar N10bn 

Date:

Gwamna Aminu Bello Masari na Jihar Katsina ya bukaci Ƙungiyar ƴan Jarida ta Ƙasa, NUJ, reshen Abuja da ta biya shi diyyar Naira biliyan 10 biyo bayan wata sanarwar manema labarai da su ka fitar, inda ya ke zargin sun ɓata masa suna.
Masari ya kuma buƙaci ‘yan jaridun da su bayar da haƙuri a hukumance a jaridun ƙasa guda takwas nan da kwanaki bakwai masu zuwa ko kuma su fuskanci hukuncin Shari’a.
Da yake zantawa da manema labarai a Katsina, a ranar Alhamis, Lauyan Masari,  E.O. Obunadike, ya ce wanda ya ke karewa ya yanke shawarar daukar irin wannan matakin ne domin kare mutuncinsa da ya gina shi ashekaru da dama.
Idan dai ba a manta ba, ‘yan jaridan biyu Emmanuel Ogbeche da Ochaika Ugwu, shugaba da sakataren  NUJ ne su ka fitar da wata sanarwa a ranar 2 ga watan Janairu, inda su ke zargin Masari ya bayar da umarnin kama Nelson Omonu na jaridar Summit Post a Abuja.
Sun yi zargin cewa gwamnan ya bayar da umarnin kama Nelson a Katsina bayan ya zarge su da ɓata masa suna.
Sai dai kuma da ga bisani Ugwu da Ogbeche sun fitar da wata sanarwa inda suka nemi gafarar Gwamna Masari, saboda sun zaci ya bada umarnin kama shi.
Amma Obunadike, ya ce haƙurin nasu bai isa ba, don haka ya ce ‘yan jaridar su bada hakurin a jaridu takwas na kasa, baya ga biyan diyyar Naira biliyan 10.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp