fidelitybank

Zargin ƙazafi: Gwamna Masari ya nemi ƴan jaridar Abuja su biya shi diyyar N10bn 

Date:

Gwamna Aminu Bello Masari na Jihar Katsina ya bukaci Ƙungiyar ƴan Jarida ta Ƙasa, NUJ, reshen Abuja da ta biya shi diyyar Naira biliyan 10 biyo bayan wata sanarwar manema labarai da su ka fitar, inda ya ke zargin sun ɓata masa suna.
Masari ya kuma buƙaci ‘yan jaridun da su bayar da haƙuri a hukumance a jaridun ƙasa guda takwas nan da kwanaki bakwai masu zuwa ko kuma su fuskanci hukuncin Shari’a.
Da yake zantawa da manema labarai a Katsina, a ranar Alhamis, Lauyan Masari,  E.O. Obunadike, ya ce wanda ya ke karewa ya yanke shawarar daukar irin wannan matakin ne domin kare mutuncinsa da ya gina shi ashekaru da dama.
Idan dai ba a manta ba, ‘yan jaridan biyu Emmanuel Ogbeche da Ochaika Ugwu, shugaba da sakataren  NUJ ne su ka fitar da wata sanarwa a ranar 2 ga watan Janairu, inda su ke zargin Masari ya bayar da umarnin kama Nelson Omonu na jaridar Summit Post a Abuja.
Sun yi zargin cewa gwamnan ya bayar da umarnin kama Nelson a Katsina bayan ya zarge su da ɓata masa suna.
Sai dai kuma da ga bisani Ugwu da Ogbeche sun fitar da wata sanarwa inda suka nemi gafarar Gwamna Masari, saboda sun zaci ya bada umarnin kama shi.
Amma Obunadike, ya ce haƙurin nasu bai isa ba, don haka ya ce ‘yan jaridar su bada hakurin a jaridu takwas na kasa, baya ga biyan diyyar Naira biliyan 10.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp