An soke tashin jiragen da aka shirya tashinsu yau da safe a filin jirgin sama na Murtala Mohammed da ke Legas, sakamakon zanga-zangar ma’aikatan filayen jiragen sama.
Lamarin ya sanya fasinjojin da suka yi sammako domin yin tafiye-tafiye cikin kunci.
Su dai ma’aikatan filayen jiragen sama na zanga-zangar ne saboda korar wasu daga cikin mambobin kungiyarsu 34 daga aiki, da kamfanin Bi-Courtney Aviation Services Limited (BASL) ya yi.
Kungiyar ma’aikatan sun yi zargin korar wasu daga cikin ma’aikatan nata da kamfanin ya yi ba ya bisa tsarin doka.
A wata sanarwa da kamfanin jirgin sama na Ibom Air, ya aikewa fasinjojinsa ya ce wannan zanga-zanga ta shafi zirga-zirgasa na yau a ciki da wajen Legas.