Tun a jiya ƙungiyoyin ‘yan kasuwa da na ‘yan uwan waɗanda aka sata a harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga watan Oktobar bara, suka sanar da shiga zanga-zangar gama gari mai haɗe da yajin aiki.
Wasu burane sun sanar da cewa su ba za su shiga zanga-zangar da yajin aikin ba, amma a larduna da yawa na Isra’ila al’amura sun tsaya cin.
Asibitoci da dama na buɗe amma ba sa aiki kamar yadda suka saba a baya, yayin da bankuna suka kasance a rufe, amma su kasuwancin na ɗaiɗaikun mutane na ci gaba da gudana.
Kamfanin dillancin labarai na Rueters ya ce an bai wasu ma’aikata damar shiga cikin yajin aikin.