fidelitybank

Zanga-zanga ta kunno kai bayan juyin mulki a Nijar

Date:

Ɗaruruwan mutane sun yi cincirindo a gaban ginin majalisar ƙasar da ke Yamai, domin nuna goyon baya ga sojoji.

Masu zanga-zangar sun buƙaci Rasha ta kawo masu ɗauki, tare da roƙon dakarun tsaron Faransa da su janye daga ƙasar.

Wasu masu zanga-zangar na ɗauke da tutar Rasha. Sai dai har yanzu babu wata alama da ke nuna wani yunƙurin shiga tsakani da Rasha ta yi.

Masu zanga-zangar sun cinna wa ofishin jami’iyar PNDS Tarayya wuta, wadda kuma ita ce jam’iyar hamɓarraen shugaban ƙasar. In ji BBC.

An jinkirta zanga-zangar nuna goyon bayan ga sojoji ne sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da aka tabka a Yamai din.

Ra’ayoyin ƴan ƙasar ya banbanta, inda wasu ke ganin juyin mulkin abu ne marar kyau, wasu kuma na ganin matakin ya yi daidai.

A ranar Laraba, ɗaruruwan magoya bayan shugaba Mohamed Bazoum, sun yi zanga-zangar adawa da matakin sojin ƙasar, sai dai dakarun tsaro sun tarwatsa su da harbin bindiga.

Magoya bayan shugaba Bazoum sun ce ba za su amince da juyin mulkin ba, sai dai babu tabbacin hanyar da za su bi wajen adawa da juyin mulkin.

Rundunar sojin Nijar ta goyi bayan juyin mulkin da sojoji suka sanar a gidan talabijin na ƙasar, inda hakan ke nuna haɗin kai tsakanin dukkan rundunonin tsaron ƙasar.

Sai dai har yanzu babu tabbacin wanda zai jagoranci gwamnatin sojin.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp