fidelitybank

Zanga-zanga ta ɓarke a kan ɗan siyasa mai tsatsauran ra’ayi a Sweden da ya ƙona Al Kur’ani

Date:

Mummunan rikici ya barke a kasar Sweden a makon nan a birnin Linköping da ke gaɓar tekun gabashin ƙasar, inda aka yi arangama tsakanin ƴan sanda da masu zanga-zanga da suka fito domin nuna fushinsu kan ƙona Al Kur’ani mai tsarki da wani dan siyasa mai tsaurin ra’ayi ya yi a wani gangaminsa.

Rahotanni sun ce, ƴan sanda uku suka jikkata.

Mutane sun sake fitowa zanga-zangar, a cewar hukumomin birnin Orebro da ke tsakiyar kasar, bayan wani gangami na nuna ƙyamar baƙi da kuma addinin Islama ƙarƙashin jagorancin mai tsattsauran ra’ayi Rasmus Paludan ɗan siyasa mai asali biyu Denmark da Sweden. A yayin zanga-zangar ‘yan sanda tara suka jikkata.

An kama mutum biyu a lokacin zanga-zangar. Ƴan sanda sun nuna cewa aikinsu shi ne su tabbatar da ƴancin mutane na bayyana ra’ayinsu, don haka ba haƙƙinsu ba ne su zaɓi wanda yake da gaskiya.

Baludan ya daɗe yana haifar da ruɗani da ce-ce-ku-ce. A watan Nuwamban 2020, hukumomin Faransa sun kama shi tare da korarsa daga ƙasar.

mmm.nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp