fidelitybank

Zanga-zanga ta ɓarke a kan ɗan siyasa mai tsatsauran ra’ayi a Sweden da ya ƙona Al Kur’ani

Date:

Mummunan rikici ya barke a kasar Sweden a makon nan a birnin Linköping da ke gaɓar tekun gabashin ƙasar, inda aka yi arangama tsakanin ƴan sanda da masu zanga-zanga da suka fito domin nuna fushinsu kan ƙona Al Kur’ani mai tsarki da wani dan siyasa mai tsaurin ra’ayi ya yi a wani gangaminsa.

Rahotanni sun ce, ƴan sanda uku suka jikkata.

Mutane sun sake fitowa zanga-zangar, a cewar hukumomin birnin Orebro da ke tsakiyar kasar, bayan wani gangami na nuna ƙyamar baƙi da kuma addinin Islama ƙarƙashin jagorancin mai tsattsauran ra’ayi Rasmus Paludan ɗan siyasa mai asali biyu Denmark da Sweden. A yayin zanga-zangar ‘yan sanda tara suka jikkata.

An kama mutum biyu a lokacin zanga-zangar. Ƴan sanda sun nuna cewa aikinsu shi ne su tabbatar da ƴancin mutane na bayyana ra’ayinsu, don haka ba haƙƙinsu ba ne su zaɓi wanda yake da gaskiya.

Baludan ya daɗe yana haifar da ruɗani da ce-ce-ku-ce. A watan Nuwamban 2020, hukumomin Faransa sun kama shi tare da korarsa daga ƙasar.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...
X whatsapp