fidelitybank

Zan yi yaƙi da duk wanda ya yi mu’amala da tsohon shugaban PDP – Wike

Date:

Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas, ya yi barazanar cewa zai yi yaki domin ganin ya gama aiki da tsohon shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Prince Uche Secondus.

Secondus dai na hannun damar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.

Wike ya yi wannan barazanar ne a ranar Asabar din da ta gabata a wajen bikin kaddamar da gina titunan cikin garin Omagwa da ke karamar hukumar Ikwerre a jihar Ribas.

Gwamnan ya ci gaba da cewa zai “gama” duk wanda ya kafa tantinsa da “makiya jihar”.

Ya ce, “Idan wani ya yaki tsarinmu, za mu yaki mutumin.

“Bari in gaya muku abin da ba ku fahimta ba a siyasa. A duk lokacin da kuka ce kuna aiki tare da mu kuma gobe kuka koma ga makiyinmu, za mu dauki dukkan karfin da muke da shi, har ma za mu bar makiyinmu mu gama da ku tukuna.

“Don haka dukkan ku da za ku koma Abuja domin yin taro da makiyanmu a jihar, zan karasa ku zuwa karshe.

“Mun tsige Shugaban Jam’iyyar na Kasa wanda bai yi kyau ba. Dukkansu suna nan, duk mun amince, yanzu za su je Abuja su yi taro da mutumin da muka cire, a tunanin za ku yi amfani da wannan wajen yakar mu, mu murkushe su”.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp