fidelitybank

Zan yi wa ADC aiki ina cikin jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Date:

Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ya ce zai bai wa shirin hadakar ‘yan hamayya cikakken haɗin kai da goyon baya don tabbatar da cewa an kawar da jam’iyyar APC a babban zaɓen 2027.

Sule Lamido, ya ce yana cikin jam’iyyar PDP daram amma zai yi wa jam’iyyar ADC aiki kamar yadda Nyesom Wike, ya ke yiwa jam’iyyar APC aiki alhali kuma ɗan PDP ne.

Tsohon gwamnan na Jigawa ya ce akwai rainin hankali dangane da yadda ake tafiyar da harkokin siyasa da abin da Wike ya ke musu a PDP, don haka shi ma dole ya marawa ADC kuma babu wanda zai rabashi da PDP.

Sule ya nuna cewa halin da Najeriya ke ciki a yanzu ba lokaci ba ne na nuna ɓangaranci ba, lokaci ne na duba wane ne ya cancanta a mara masa baya ba tare da la’akari da jam’iyya ba.

Ya ce batun Jam’iyya ya haifar da tarin kalubale da matsaloli na ɓangaranci da rabuwar kawuna a Najeriya wanda dole ne a warware hakan.

Ya ce duk matsalolin PDP haddasata aka yi, don haka babu inda zai je, kuma babu wanda ya ke tsoro ko nuna munafurci.

Ya ce abubuwa da dama ana sa son zuciya a ciki, don haka shi ya san tsarin da zai bi saboda al’umma ce a gabansa. Kuma dole ya yi aiki domin kare PDP da bai wa ADC ƙasar.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp