fidelitybank

Zan yi wa ADC aiki ina cikin jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Date:

Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ya ce zai bai wa shirin hadakar ‘yan hamayya cikakken haɗin kai da goyon baya don tabbatar da cewa an kawar da jam’iyyar APC a babban zaɓen 2027.

Sule Lamido, ya ce yana cikin jam’iyyar PDP daram amma zai yi wa jam’iyyar ADC aiki kamar yadda Nyesom Wike, ya ke yiwa jam’iyyar APC aiki alhali kuma ɗan PDP ne.

Tsohon gwamnan na Jigawa ya ce akwai rainin hankali dangane da yadda ake tafiyar da harkokin siyasa da abin da Wike ya ke musu a PDP, don haka shi ma dole ya marawa ADC kuma babu wanda zai rabashi da PDP.

Sule ya nuna cewa halin da Najeriya ke ciki a yanzu ba lokaci ba ne na nuna ɓangaranci ba, lokaci ne na duba wane ne ya cancanta a mara masa baya ba tare da la’akari da jam’iyya ba.

Ya ce batun Jam’iyya ya haifar da tarin kalubale da matsaloli na ɓangaranci da rabuwar kawuna a Najeriya wanda dole ne a warware hakan.

Ya ce duk matsalolin PDP haddasata aka yi, don haka babu inda zai je, kuma babu wanda ya ke tsoro ko nuna munafurci.

Ya ce abubuwa da dama ana sa son zuciya a ciki, don haka shi ya san tsarin da zai bi saboda al’umma ce a gabansa. Kuma dole ya yi aiki domin kare PDP da bai wa ADC ƙasar.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dangote ya rage farashin litar mai zuwa ₦820

Kamfanin matatar man Dangote ya rage farashin litar mai...

Dubai ta sake tsaurara matakan bai wa ‘yan Najeriya biza

Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, UAE ta sake sanya wasu dokoki...

‘Yan Bindigar Katsina ‘yan asalin jihar mu ne – Gwamna

Gwamnan Katsina Umaru Dikko Radda ya ce galibin 'yan...

Zan yi wa ADC aiki ina cikin jam’iyyar PDP – Sule Lamido

Jigo a babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya...

Buhari da Tinubu kan su a hade ya ke – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari...

Ganduje ya kama aiki a hukumar kula da filayen jirgin sama

Tsohon shugaban jam'iyyar APC mai mulki, Abdullahi Ganduje, ya...

JAMB ta amince da maki 150 mafi ƙanƙanta don samun gurbin karatu a jami’o’i

Hukumar shirya jarrabawar shiga Jami'o'i ta Najeriya (JAMB) ta...

ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Ƙungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya, ASUU da dakatar yajin...

Masu haɗakar ADC na ɓaɓatu ne saboda rashin gwamnati – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umar Radda ya yi...

Ba ruwan Biri da gada a makamin Nukiliya – Shettima

Mataimakin shugaba Najeriya Kashim Shettima ya ce ƙasar za...

An kashe Mutane 70 a jihar Filato

Rahotonni daga jihar Filato na cewa ƴanbindiga sun kai...

Ambaliya ta kashe mutane 100 a Amurka

Hukumomi a jihar Tesxas da ke Amurka sun bayyana...
X whatsapp