Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebolo a ranar Talata ya yi alkawarin yin hadin gwiwa da gwamnatin tarayya, kamfanoni masu zaman kansu, kungiyoyi masu zaman kansu, wadanda ke kasashen waje, da sauran masu ruwa da tsaki, domin bunkasa dukkanin sassan tattalin arzikin jihar.
Okpebholo ya yi wannan alkawarin ne a jawabinsa na farko jim kadan bayan rantsar da shi a matsayin gwamnan jihar.
Sabon Gwamnan da aka rantsar wanda ya yi nuni da cewa, halin da tituna ke ciki ya sanya jama’a ke da wahala wajen kaura daga wannan yanki zuwa wancan, ya yi alkawarin cewa nan da nan gwamnatinsa za ta fara aiki don ganin an sake bi hanyoyin.
Ya kara da cewa, wani bangare na ajandarsa shi ne, samar da ababen more rayuwa, da gina magudanan ruwa da gadoji, domin saukaka harkokin sufuri ga kowa da kowa.
Ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta tallafa wa masu kananan sana’o’i da kuma mata masu kasuwa da rance mai sauki.
Ya kuma bayyana shirin gwamnatin sa na daukar malamai da sake gina ajujuwan da ba su da kyau a fadin jihar.
“Gwamnatina za ta gaggauta daukar matakin daukar malamai da sake gina ajujuwan da suka lalace. Za a kuma karfafa ilimin manyan makarantu ta hanyoyi da dama, don tabbatar da ingantaccen ilimi.
“Ba za a bar mu da yawan matasan mu ba. Za mu tallafa musu don samun dabarun da suka dace don karfafa kansu,” in ji shi.
Ya ce gwamnatinsa a shirye ta ke ta hada al’ummomin da har yanzu ba a hada su da wutar lantarki ta kasa ba, don tabbatar da sun samu wutar lantarki.