fidelitybank

Zan yi mulkin gaskiya da ƙanƙastar da kai – Matashin shugaban kasar Senegal

Date:

Zaɓaɓɓen shugaban Senegal Bassiorou Diomaye ya yi alƙawarin yin mulki tare da ƙanƙastar da kai da kuma nuna gaskiya.

Ya bayyana haka ne a jawabinsa na farko bayan zaɓen shugaban ƙasar da aka yi ranar Lahadi.

Babban abokin hamayyar Mista Faye daga jam’iyya mai mulki Amadou Ba tuni ya amince da shan kaye abin da ya sa Faye mai shekara 44 ya zama shugaban ƙasa mafi ƙanƙantar shekaru a tarihin ƙasar.

“Zaɓe na da aka yi ya nuna al’ummar Senegal sun amince su tsame kansu daga abubuwan da suka faru a baya,” kamar yadda ya faɗa wa ƴan jarida a ranar Litinin.

“Na yi alƙawarin yin shugabanci tare da ƙanƙan da kai da kuma gaskiya.”

Ɗaya daga cikin manyan ƙudurorinsa a matsayin shugaban ƙasa shi ne “haɗa kan ƴan kasa” sakamakon yadda aka shafe shekara uku ana tashin hankali da kuma rikicin siyasa a ƙasar, kamar yadda Mista Faye ya bayyana. In ji BBC.

Ya kuma yi alƙawarin “yaƙar cin hanci a kowane mataki” da sake gina hukumomi tare da magance matsalar tsadar rayuwa.

Mista Faye ya kuma gode wa shugaba Macky Sall mai barin gado ganin yadda ya taimaka aka gudanar da zaɓe cikin cikin nasara.

Sakamakon zaɓen wanda ba na hukuma ba ya nuna Mista Faye ne ke kan gaba da kusan kashi 53.7 cikin 100 yayin da Mista Ba yake da kashi 36.2 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa.

Nasararsa na zuwa ne ƙasa da mako biyu bayan da aka sake shi daga gidan yari.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp