Dan takarar shugaba kasa a zaben badi karkashin Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya karbi wata tawagar yayan Jam’iyyar PDP daga jihar Zamfara karkashin jagorancin Dr. Dauda Lawan Wanda shi ne Dan Takarar gwamnan jihar na PDP.
Kazalika cikin tawagar da ta ziyarci Wazirin na Adamawa sun hada da yan siyasar nan na APC da suka sauya sheka zuwa PDP Alhaji Salihu Mai Buhu Gummi da Alhaji I. Alhaji Bakuraa Sahabi Liman Kaura.
A jawabin sa, jagoran ayarin ya ce, sun gamsu da akidun siyasar tsohon mataimakin shugaban kasar saboda kishin sa da kwazo da kuma manufarsa ta kaunar hada kan kasa da zaman lafiya da ci gaba, inda suka tabbatar wa da Dan Takarar ta PDP goyon bayan su a yunkurin sa na Gina ingantacciiyar kasa.
A nasa bangare, Atiku Abubakar, yayin da yake gode musu bisa ziyarar, ya sake jaddada aniyar sa ta aiki tare da yayan Jam’iyyar da masu ruwa da tsaki a Zamfara da Najeriya gaba daya domin samun nasarar Jam’iyyar PDP a zaben 2023.