Dan takarar shugaban kasa kuma Ministan Neja Delta, Godswill Akpabio ya yi alkawarin ci gaba da yaki da cin hanci da rashawa ta hanyar amfani da tsarin shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Ministan ya bayyana cewa gwamnati ba za ta iya yaki da cin hanci da rashawa ba idan ba ta yi yaki da fatara da karfi ba, yana mai cewa batutuwan biyu tagwaye ne.
Ya yi nuni da cewa idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa, zai yi amfani da shirye-shiryen zuba jari na Social Investment don magance talauci kamar yadda gwamnatin Buhari ke amfani da shi.
Akpabio, wanda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a ranar Laraba a garin Uyo, ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Channels a ranar Alhamis.
Tsohon gwamnan Akwa Ibom ya kara da cewa zai yi amfani da albarkatun dan adam da na kasa wajen tabbatar da ci gaba idan aka zabe shi a matsayin shugaban Najeriya na gaba.