fidelitybank

Zan tsoma baki tsakanin Natasha da Majalisa – Ministar Mata

Date:

Ministar al’amuran mata da walwalar jama’a, Imaan Suleiman ta ce, a shirye take ta shiga domin sasanta rikicin dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar Kogi ta tsakiya.

Yayin da take jawabi ga manema labarai a fadar shugaban ƙasar ranar Juma’a, ministar ta bayyana takaicinta kan zargin cin zarafin lalatar da aka yi a majalisar dattawan, lamarin da ta bayyana da ”abin takaici”.

Tana mai cewa bai kamata irin wannan abu ya riƙa faruwa a majalisar dokokin Najeriya ba.

Imaan Sulaiman ta ce ma’aikatarta za ta tattauna da majalisar dattawan domin duba yadda za a sasanta matsalar cikin salama.

“Za mu sasanta batun. Za mu tattauna da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da sasanci cikin kwanciyar hankali.”

A ranar Alhamis ne Majalisar Dattawan Najeriya ta dakatar ta dakatar da Sanata Natasha na tsawon wata shida, saboda saɓanin da ya shiga tsakaninta da shugaban majalisar, kan sauya mata wurin zama, inda daga baya ya koma zargin cin zarafin lalata.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp