Tsohon gwamnar Jihar Anambra, Peter Obi, ya ce, zai tsaya takarar shugabancin kasa har idan jamâiyyarsa ta PDP ta bai wa yankin Kudu tikiti.
Obi, wanda ya yi wa PDP takarar mataimakin shugaban kasa a 2019, tare da Atiku Abubakar, ya bayyana hakan ne a sakon da ya wallafa a shafin sa na twitter a ranar Talata.
Ya ce, âEh tabbas zan tsaya takarar shugabancin Najeriya, domin samun damar yi wa kasa ta hidima a matsayin shugaban kasa, idan har jamâiyyar PDP ta kai tikitin Kudu”. In ji Peter.
Sanarwar ta Obi na zuwa ne kasa da sa’a 24, bayan da gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya tabbatar da tsayawa takarar shugaban kasa karkashin jamâiyyar PDP.