fidelitybank

Zan tabbatar da adalci a majalisar dokokin jihar Rivers – Sabon Shugaba

Date:

Majalisar dokokin jihar Rivers ta zaɓi Edison Ehie a matsayin kakakinta.

Zaɓen nasa ya gudana ne a yayin zaman majalisar, inda ‘yan majalisar 26 suka kada kuri’ar amincewa da shi.

Wannan hukuncin ya biyo bayan dakatarwar da aka yi wa wasu manyan shugabannin majalisar.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa bayyanar Ehie a matsayin sabon shugaban majalisar ya biyo bayan da ‘yan majalisar guda 26 suka tsige magabacinsa, Martins Amaehule,

Da yake zantawa da manema labarai bayan zaben sa, Ehie ya bayyana jin daɗinsa ga abokan aikinsa da suka ɗora masa alhakin jagorantar majalisar.

“Alƙawarina ga mutanen Rivers shine zan kasance mai adalci ga kowa da kowa; Zan tabbatar da bin doka da oda.

“Ba zan ci amanar abokan aikina ba. Ba zan ci amanar mutanen Rivers ba. Ba zan ci amanar mazaba ta ba.”

“Zan tabbatar da ‘yancin cin gashin kan Majalisar Dokokin Jihar Ribas, tare da mutunta juna ga bangaren shari’a da bangaren zartarwa na gwamnati,” inji shi.

Bugu da kari, sabon kakakin ya bayyana cewa zai tabbatar da cewa ‘yan majalisar da aka dakatar sun samu sahihin saurare ta hanyar kwamitin koke.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp