fidelitybank

Zan sanya hannu a kashe wanda ya kashe Daliba Hanifa – Gwamnan Kano

Date:

Watanni biyar bayan da aka yankewa malamin makarantar nan Abdulmalik Tanko, hukuncin kisa, bisa samunsa da laifin kashe daliba Hanifa Abubakar mai shekaru biyar, tuni dai Gwamna Abba Yusuf, ya sha alwashin ganin an zartar da hukuncin kisa ga wanda ake tuhuma.

Gwamnan ya ce, dole ne a aiwatar da hukuncin da kotu ta yanke.

Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka ne a yayin wani taron tunawa da ranar yara ta duniya ta 2024 a Kano.

Wata babbar kotun jihar Kano ta yanke wa Abdulmalik Tanko da wanda ake zargin Hashimu Ishyaku hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan ta same su da laifin kisan Hanifa.

Gwamnan ya ce, tabbatar da cewa, wadanda aka yankewa hukuncin kisa sun gurbi abun da suka shuka, ta hanyar ne kadai zai zama izina ga masu neman aikata irin wannan laifin.

A cewarsa, jihar na gab da ayyana dokar ta baci kan ilimi domin tabbatar da ingantaccen ilimi ga yara a Kano.

Gwamnan ya kuma yi alkawarin cewa, nan da wani lokaci, za a fara ciyarwa a makarantu kyauta da kuma bayar da tufafi kyauta ga yara ‘yan makaranta daga ajin firamare na daya har zuwa aji.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp