Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce ba shi da nadama kan goyon bayan da ya baiwa Shugaba Bola Tinubu a zaben 2023.
Kafin a nada shi minista, Wike ya kasance gwamnan Jihar Rivers na tsawon shekaru takwas a karkashin jamâiyyar Peoples Democratic Party (PDP).
Shugaba Tinubu daga baya ya gayyace shi ya zama Ministan FCT a cikin gwamnatin tarayya karkashin jagorancin jamâiyyar All Progressives Congress (APC).
Wike ya yi wannan maganar ne a lokacin da yake halartar bikin godiya da PDP ta shirya a karamar hukumar Ahoada East da West na jihar, inda yayi godiya ga Shugaba Tinubu bisa yarda da shi.
Ya ce kafin zaben shugaban kasa, an yi masa barazanar saboda goyon bayan da ya baiwa Tinubu, amma yana mai cewa zai yi hakan nan gaba idan wata dama ta taso.
A cewarsa:âBan yi nadama ba, Idan wata dama ta taso, zan kara yin haka.â