Wani jigo a jam’iyyar PDP a karamar hukumar Warri ta Kudu a jihar Delta, Victor Umukoro ya ce, shi da wasu irinsa za su ruguza jam’iyyar tare da sake gina ta domin inganta Nijeriya.
Ya yi wannan jawabi ne ga dan takarar Sanatan Delta ta Kudu na jam’iyyar New Nigerian People’s Party, NNPP, Omatseye Nesiama a wani taro na gari da NNPP ta shirya a Warri.
Ya ce, “Ni dan PDP ne. Ni dan PDP ne abin da na fada ya isa haka. Zamu ruguza wannan PDP, mu sake gina PDP domin sabuwar Najeriya.
Tsohon dan takarar shugabancin karamar hukumar Warri ta Kudu ya ce wasu ‘yan jam’iyyar sun fusata saboda kazantar siyasar da ake zargin ana tafkawa a jam’iyyar.
“Suna ce maka Oga ya gama magana. Tsarin yayi magana. Mun gaji. Za mu kawo karshensa.”
Umukoro ta ce mutane irin su Omatseye Nesiama ne wadanda suka samu horo sosai kuma sun yi balaguro da su ke bukata a matsayinsu na wakilai.
“A dalilin zaben nan, ni ba dan jam’iyya ba ne. Ni mai kallo ne.”
Karanta Wannan: Shugaban PDP a Yobe ya koma APC
Umukoro, ya yi korafin cewa suna da koma-baya a siyasance a tsarin Essi da ke Warri, tare da yin kira ga al’ummar yankin da kada su ji tsoron duk wata barazana a lokacin zabe mai zuwa amma su fito baki daya su zabi Omatseye Nesiama.
Tun da farko, Omatseye Nesiama ya tabbatar da cewa har yanzu yana nan a takarar kuma babu gudu babu ja da baya, yana mai shan alwashin cewa a shirye yake ya yi aiki tare da kawo sauyi a majalisar dattawa.