fidelitybank

Zan ruguza PDP da ‘yan cikinta – Dan PDP a jawabin taron nnpp

Date:

Wani jigo a jam’iyyar PDP a karamar hukumar Warri ta Kudu a jihar Delta, Victor Umukoro ya ce, shi da wasu irinsa za su ruguza jam’iyyar tare da sake gina ta domin inganta Nijeriya.

Ya yi wannan jawabi ne ga dan takarar Sanatan Delta ta Kudu na jam’iyyar New Nigerian People’s Party, NNPP, Omatseye Nesiama a wani taro na gari da NNPP ta shirya a Warri.

Ya ce, “Ni dan PDP ne. Ni dan PDP ne abin da na fada ya isa haka. Zamu ruguza wannan PDP, mu sake gina PDP domin sabuwar Najeriya.

Tsohon dan takarar shugabancin karamar hukumar Warri ta Kudu ya ce wasu ‘yan jam’iyyar sun fusata saboda kazantar siyasar da ake zargin ana tafkawa a jam’iyyar.

“Suna ce maka Oga ya gama magana. Tsarin yayi magana. Mun gaji. Za mu kawo karshensa.”

Umukoro ta ce mutane irin su Omatseye Nesiama ne wadanda suka samu horo sosai kuma sun yi balaguro da su ke bukata a matsayinsu na wakilai.

“A dalilin zaben nan, ni ba dan jam’iyya ba ne. Ni mai kallo ne.”

Karanta Wannan: Shugaban PDP a Yobe ya koma APC

Umukoro, ya yi korafin cewa suna da koma-baya a siyasance a tsarin Essi da ke Warri, tare da yin kira ga al’ummar yankin da kada su ji tsoron duk wata barazana a lokacin zabe mai zuwa amma su fito baki daya su zabi Omatseye Nesiama.

Tun da farko, Omatseye Nesiama ya tabbatar da cewa har yanzu yana nan a takarar kuma babu gudu babu ja da baya, yana mai shan alwashin cewa a shirye yake ya yi aiki tare da kawo sauyi a majalisar dattawa.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp