fidelitybank

Zan ruguza PDP da ‘yan cikinta – Dan PDP a jawabin taron nnpp

Date:

Wani jigo a jam’iyyar PDP a karamar hukumar Warri ta Kudu a jihar Delta, Victor Umukoro ya ce, shi da wasu irinsa za su ruguza jam’iyyar tare da sake gina ta domin inganta Nijeriya.

Ya yi wannan jawabi ne ga dan takarar Sanatan Delta ta Kudu na jam’iyyar New Nigerian People’s Party, NNPP, Omatseye Nesiama a wani taro na gari da NNPP ta shirya a Warri.

Ya ce, “Ni dan PDP ne. Ni dan PDP ne abin da na fada ya isa haka. Zamu ruguza wannan PDP, mu sake gina PDP domin sabuwar Najeriya.

Tsohon dan takarar shugabancin karamar hukumar Warri ta Kudu ya ce wasu ‘yan jam’iyyar sun fusata saboda kazantar siyasar da ake zargin ana tafkawa a jam’iyyar.

“Suna ce maka Oga ya gama magana. Tsarin yayi magana. Mun gaji. Za mu kawo karshensa.”

Umukoro ta ce mutane irin su Omatseye Nesiama ne wadanda suka samu horo sosai kuma sun yi balaguro da su ke bukata a matsayinsu na wakilai.

“A dalilin zaben nan, ni ba dan jam’iyya ba ne. Ni mai kallo ne.”

Karanta Wannan: Shugaban PDP a Yobe ya koma APC

Umukoro, ya yi korafin cewa suna da koma-baya a siyasance a tsarin Essi da ke Warri, tare da yin kira ga al’ummar yankin da kada su ji tsoron duk wata barazana a lokacin zabe mai zuwa amma su fito baki daya su zabi Omatseye Nesiama.

Tun da farko, Omatseye Nesiama ya tabbatar da cewa har yanzu yana nan a takarar kuma babu gudu babu ja da baya, yana mai shan alwashin cewa a shirye yake ya yi aiki tare da kawo sauyi a majalisar dattawa.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp