fidelitybank

Zan rufe duk wani banki da ya bijirewa umarnin CBN – Soludo

Date:

Gwamnan jihar Anambra, Charles Soludo, ya umarci mazauna jihar da su ci gaba da amfani da tsofaffin takardun naira 200 da 500 da 1,000 tare da sababbin takardun kuɗin a ko’ina cikin jihar.

Cikin wata sanarwa ta musamman da Charles Soludo wanda tsohon gwamnan babban banki ne, ya ce, babban bankin ƙasa ya umarci bankunan kasuwanci a ƙasar da su ci gaba da biyan masu ajiyar kuɗi a bankunan da tsofaffin takardun kuɗi.

Sannan kuma su ci gaba da karɓar tsofaffin takardun kuɗin a duk lokacin da aka gabatar da su.

Karanta Wannan: Sai na kulle duk wani banki da kantin da ya ki karbar tsofaffin kudi – Gwamnan Ogun

Gwamnan jihar ta Anambra ya ce, ya tabbatar da sahihancin umarnin yayin wata hira da ya yi da gwamnan babban bankin Godwin Emefiele ta wayar tarho a ranar lahadi da daddare.

Soludo ya ce, gwamnan CBN ya bayar da wannan umarnin ne yayin wani taro da babban bankin ya yi da bankunan ƙasar da aka yi a ranar Lahadi 12 ga watan Maris.

Gwamnan na Anambra ya kuma buƙaci al’ummar jihar da su kai ƙarar dukkan bankin da ya ƙi bin umarnin babban bankin na biya da karɓar tsofaffin takardun kuɗin.

Ya na gargaɗin cewa gwamnatinsa za ta rufe duk bankin da ya bijire wa wannan umarnin.

A ranar 3 ga watan Maris ne kotun ƙolin Najeriya ya yanke hukuncin ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin ƙasar har zuwa 31 ga watan Disamban 2023.

Wasu jihohin kasar ne dai suka shigar da ƙara a gaban kotun, suna neman a ɗage wa’adin da CBN ya sanya na daina amfani tsofaffin kuɗin.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp