Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana shirinsa na halartar wasu gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC, gabanin zaben watan Fabrairu.
Buhari ya nuna jajircewar sa bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya sha suka kan rashin halartar taron yakin neman zaben jam’iyyar.
Wata sanarwa da kakakin yakin neman zaben Tinubu/Shettima, Festus Keyamo, ya fitar ta ce Buhari zai jagoranci gangamin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a jihohin Legas, Imo, Katsina, da kuma wasu jihohi bakwai.
Jadawalin da Keyamo ya fitar a ranar Alhamis ya sanya jihar ta hada da: Adamawa ranar 9 ga watan Janairu; Jihar Yobe ranar 10 ga watan Janairu; Jihar Sokoto ranar 16 ga watan Janairu; Jihar Kwara a ranar 17 ga Janairu; Jihar Ogun a ranar 25 ga watan Janairu; Jihar Cross River a ranar 30 ga Janairu; Jihar Nassarawa a ranar 4 ga Fabrairu; Jihar Katsina a ranar 6 ga Fabrairu; Jihar Imo a ranar 14 ga Fabrairu da kuma Grand Finale a jihar Legas a ranar 18 ga Fabrairu.
Ko Buhari ma ba shi da kwarin gwiwa a kan Tinubu – Atiku
Keyamo ya yi kira ga ‘ya’yan jam’iyyar APC da magoya bayan Tinubu da su fito gadan-gadan domin gudanar da gangamin yakin neman zaben da za a yi.
“Sa’ar sifili ta kusa; dole ne ruhinmu ya zama babba; Kada mu ja da baya a wannan tattakin na hadin gwiwa zuwa ga nasararmu da Allah ya kaddara,” in ji sanarwar.