Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Mista Ayodele Fayose ya ce, zai nada Ministan kula da ababen more rayuwa na Ciki wato Tumbi, idan ya zama shugaban Najeriya.
Fayose ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan, bayan bayyanar sa a gaban kwamitin tantance shugaban kasa na jam’iyyar PDP a Abuja, ranar Juma’a.
A lokacin da kwamitin ya tambaye shi manufofinsa na samar da ababen more rayuwa a cikinsa, ya bayyana karara cewa hakan na daga cikin manufofinsa idan ya zama shugaban kasa.
“Na bayyana karara cewa zan sami minista mai kula da kayayyakin ciki da jin dadin jama’a,” in ji shi.
Sai dai ya kara da cewa, idan aka yi la’akari da yadda kwalta da samar da sauran ababen more rayuwa na da kyau, hakan ba zai wadatar da ‘yan kasa da ke fama da yunwa ba.
“Don haka, a gare ni, ababen more rayuwa na ciki wani bangare ne na tallafawa talakawan Najeriya. Ayyukan ciki a karkashin kulawata a matsayina na shugaban Najeriya zai zama babban jigo.