Tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi wannan alkawarin ne a taron tattalin arziki na kamfanoni masu zaman kansu kan zaben shugaban kasa na 2023, wanda kungiyar ‘yan kasuwa da masana’antu ta Legas ta shirya a Commerce House da ke Victoria Island Legas ranar Talata.
A jawabin da shugaban kungiyar, Dr Michael Olawale Cole ya gabatar, ya yi wa mahalarta maraba sosai tare da bayyana matsayin LCCI da aka kafa a shekarar 1888 a matsayin babbar cibiyar kasuwanci da masana’antu a yammacin Afirka, wanda ke wakiltar sama da kashi 70 na kungiyoyi na masu zaman kansu a Najeriya.
A cikin jawabinsa, shugaban ya bayyana cewa “yayin da majalisar ba ta cikin jam’iyya, duk da haka muna da sha’awar ajandar tattalin arziki na ‘yan takara da kuma shirye-shiryensu na samar da ingantacciyar Najeriya a nan gaba”.
Ya yi alkawarin cewa mambobin kungiyar LCCI suna son bayar da gudummawa wajen kafa wani sabon tsarin tattalin arziki wanda zai iya kawar da tattalin arzikin Najeriya daga kangi, sannan ya kara jaddada cewa taron ya zama dole domin fitar da sabbin tsare-tsare, gyare-gyaren hukumomi da ingantaccen shugabanci a matsayin muhimman abubuwan da za a samar da su a wani sabon tsarin tattalin arziki a Najeriya.