Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatarwa ‘yan asalin jihar Zamfara cewa, zai mayar da hankali kan harkar noma da ma’adanai, domin bunkasa tattalin arzikin jihar idan aka zabe shi a zabe mai zuwa.
A cewarsa, ci gaban sassan gaba daya zai samar da karin guraben ayyukan yi da za su iya rage yawaitar aikata miyagun laifuka a jihar.
Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin yakin neman zabensa a harabar baje kolin kasuwanci da ke Gusau, babban birnin jihar, inda ya ce duk da wannan zagon kasa, APC za ta gudu da nasara a duk zabe.
Ya ci gaba da cewa, ba ya je jihar Zamfara domin yakin neman zabe, sai dai ya yi godiya ga jama’a saboda dimbin goyon bayan da suke ba jam’iyyar tun bayan da Nijeriya ta dawo mulkin dimokuradiyya a hannun sojoji a 1999.
A cewarsa, jihar Zamfara ta samu albarkatun mutane da na kasa wadanda ke bukatar ci gaba domin bunkasa tattalin arzikin kasa da jihar baki daya.
Ya yabawa Gwamna Matawalle da tsohon Gwamna Ahmad Sani Yarima da tsohon Gwamna Aliyu Mahamud Shinkafi da tsohon Gwamna Abdul Aziz Yari bisa gudunmawar da suka bayar wajen ganin APC ta kasance karkashin inuwa daya a jihar.
“Har yanzu zan dawo jihar Zamfara domin yin biki na musamman idan lokaci ya yi,” in ji shi.