fidelitybank

Zan mayar da hankali bangaren noma da ma’adanai a Zamfara – Tinubu

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatarwa ‘yan asalin jihar Zamfara cewa, zai mayar da hankali kan harkar noma da ma’adanai, domin bunkasa tattalin arzikin jihar idan aka zabe shi a zabe mai zuwa.

A cewarsa, ci gaban sassan gaba daya zai samar da karin guraben ayyukan yi da za su iya rage yawaitar aikata miyagun laifuka a jihar.

Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin yakin neman zabensa a harabar baje kolin kasuwanci da ke Gusau, babban birnin jihar, inda ya ce duk da wannan zagon kasa, APC za ta gudu da nasara a duk zabe.

Ya ci gaba da cewa, ba ya je jihar Zamfara domin yakin neman zabe, sai dai ya yi godiya ga jama’a saboda dimbin goyon bayan da suke ba jam’iyyar tun bayan da Nijeriya ta dawo mulkin dimokuradiyya a hannun sojoji a 1999.

A cewarsa, jihar Zamfara ta samu albarkatun mutane da na kasa wadanda ke bukatar ci gaba domin bunkasa tattalin arzikin kasa da jihar baki daya.

Ya yabawa Gwamna Matawalle da tsohon Gwamna Ahmad Sani Yarima da tsohon Gwamna Aliyu Mahamud Shinkafi da tsohon Gwamna Abdul Aziz Yari bisa gudunmawar da suka bayar wajen ganin APC ta kasance karkashin inuwa daya a jihar.

“Har yanzu zan dawo jihar Zamfara domin yin biki na musamman idan lokaci ya yi,” in ji shi.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp