Fitaccen jarumin nan a masana’antar fina-finai ta Kannywood, wanda kuma shi ne sabon shugaban hukumar kula da fina-finai ta Najeriya, Ali Nuhu, ya ce zai mayar da hankali kan wasu manyan sauye-sauye guda uku a hukumar da zai jagoranta.
A watan da ya gabata ne dai shugaba Bola Tinubu ya nada shi a matsayin shugaban hukumar.
Za a iya cewa dai Ali Nuhu ne jarumi na farko daga arewacin Najeriya da ya samu irin wannan dama ta jagorantar hukumar da ke kula da masana’antar da ya fito daga cikintat.