Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya sha alwashin mara wa matasa masu kaifin basira baya, dazarar su ka ɗare manyan kujeru a babban taron jam’iyyar APC dake tafe.
Buhari ya umarci shugaban ma’aikatan fadarsa da sakataren gwamnati su tabbatar an saka matasa a wasu wurare na gwamnatinsa.
Shugaban ƙasa Buhari ya yi wannan furucin ne yayin da kungiyar haɗin kan matasan APC suka kai masa ziyara fadarsa a ranar Jumu’a.
Muhammadu Buhari, ya tabbatar wa da matasan APC cewa, zai goyi bayan zakakurai daga cikinsu, muddin su ka ɗare kan manyan muƙamai a taron APC.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa, Buhari ya sha alwashin marawa matasan baya su samu mukamai a shugabancin APC na ƙasa a taron ranar 26 ga watan Fabrairu, 2022 da za su yi.