fidelitybank

Zan marawa gwamnatin APC baya a Ekiti – Fayose

Date:

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya sha alwashin marawa zababben gwamnan jihar, Biodun Oyebanji baya domin ci gaban jihar Ekiti.

Wannan dai na zuwa ne a daidai ranar da ya mayar da goyon bayansa na tsayawa takarar shugabancin kasa a kudancin kasar duk da cewa, jam’iyyarsa ta PDP ta gabatar da dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar wanda ya fito daga yankin Arewa.

Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake karbar bakuncin Oyebanji, wanda ya kai masa ziyara, bayan lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Yuni a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress.

Kalaman Fayose: “Na yi alkawari zan goyi bayan gwamnatin Oyebanji a kowane fanni da za a bukaci goyon bayansa. Ci gaban jihar Ekiti kokari ne na hadin gwiwa.

“Dole ne ku kalli duk mutanen Ekiti a matsayin naku. Kai ne gwamnan kowa ba tare da la’akari da siyasa ba”.

A halin da ake ciki, Oyebanji ya ce, ya kai ziyarar ne domin mika gaisuwa ga Fayose a matsayinsa na tsohon gwamnan jihar, wanda a cewarsa, ya nuna kishin kasa ta hanyar taya shi murna jim kadan bayan bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Yuni.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp