Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya sha alwashin marawa zababben gwamnan jihar, Biodun Oyebanji baya domin ci gaban jihar Ekiti.
Wannan dai na zuwa ne a daidai ranar da ya mayar da goyon bayansa na tsayawa takarar shugabancin kasa a kudancin kasar duk da cewa, jam’iyyarsa ta PDP ta gabatar da dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar wanda ya fito daga yankin Arewa.
Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake karbar bakuncin Oyebanji, wanda ya kai masa ziyara, bayan lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Yuni a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress.
Kalaman Fayose: “Na yi alkawari zan goyi bayan gwamnatin Oyebanji a kowane fanni da za a bukaci goyon bayansa. Ci gaban jihar Ekiti kokari ne na hadin gwiwa.
“Dole ne ku kalli duk mutanen Ekiti a matsayin naku. Kai ne gwamnan kowa ba tare da la’akari da siyasa ba”.
A halin da ake ciki, Oyebanji ya ce, ya kai ziyarar ne domin mika gaisuwa ga Fayose a matsayinsa na tsohon gwamnan jihar, wanda a cewarsa, ya nuna kishin kasa ta hanyar taya shi murna jim kadan bayan bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Yuni.