fidelitybank

Zan kori duk ma’aikacin da bai dawo daga yajin aiki ba nan da awa 72 – Gwamnan Ebonyi

Date:

Gwamnan jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, ya yi barazanar sallamar duk wani ma’aikacin da ya shiga yajin aiki nan da awa 72 idan bai koma aiki ba.

 

Gwamna Nwifuru ya bayyana haka ne a ranar Litinin a ofishinsa da ke Abakaliki a lokacin da yake jawabi a game da yajin aikin da shugaban ƙungiyar ƙwadago na jihar, Kwamrade Comrade Oguguo Egwu ya fitar, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

 

A ranar Lahadi ne Oguguo ya bayyana cewa yajin aikin biyayya ce ga umarnin shugaban ƙungiyar na ƙasa na ranar 8 ga Nuwamban 2024, inda ta yi kira ga ma’aikata a duk jihar da ba a fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi ba su shiga yajin aiki.

 

Nwifuru, ya ce majalisar tarayya ba ta ƙayyyade sabon albashi ba, inda a cewarsa dokar ta yi magana ne kan mafi ƙarancin albashi.

 

“Na fara biyan sabon mafi ƙarancin albashi tun a watan Oktoba, shi ya sa na yi mamaki da na ga sun fara yajin aiki. Kuma babu wani ma’aikaci da yake binmu bashin albashi, haka ma ƴan fansho.

 

“Don haka duk wanda bai koma aiki ba nan da awa 72, zan sallame shi, in ɗauki wasu.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa ya bayar da umarnin a fara ɗaukar sunayen waɗanda suke zuwa aiki, sannan ya ce babu maganar zaman sulhu, “saboda kwamrade Egwu ba ma’aikacinmu ba ne.”

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp