Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Bola Tinubu, ya ce, zai tunkari matsalar cin hanci da rashawa idan aka zabe shi shugaban kasa a zabe mai zuwa.
Tinubu ya ba da wannan tabbacin ne a ranar Alhamis yayin wani taron tuntuba da kungiyar masana’antun gine-gine ta kasa, FOCI, a Abuja.
Ya ce, gwamnatinsa za ta goyi bayan kafa bankin gine-gine.
Tsohon gwamnan na Legas ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnatinsa za ta yi amfani da dabarun da za su jawo hankalin masu zuba jari, maimakon tsoratar da masu zuba jari ta hanyar da nufin kawar da cin hanci da rashawa daga tsarin Najeriya.
Tinubu ya ce, “Ba ma so mu tsoratar da masu zuba jari na yau da gobe, amma mun yi muku alkawari, za mu kawar da cin hanci da rashawa. Wani bangare na shi shi ne mu kalli kanmu ma. Ba tilastawa kawai ba amma don rage girman cin hanci da rashawa.”