Gwamnan jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa, ya yi alkawarin dorawa ga ayyukan magajinsa, Marigayi Oluwarotimi Akeredolu.
Aiyedatiwa ya bayyana haka ne a yayin wani tattakin kyandir da ‘yan kungiyar lauyoyin Najeriya NBA reshen jihar Ondo suka shirya domin karrama marigayi Akeredolu a gidan gwamnati dake Akure a daren Juma’a.
Ya bayyana Akeredolu a matsayin hazikin shari’a maras tsoro kuma shugaba mai kwazo.
A cewarsa, jajircewar Akeredolu na yin adalci da yiwa jama’a hidima ya sa aka ba shi mukamin “Babban Lauyan Talakawa.”
“Abin da kuka yi a wannan dare abin yabawa ne; yana nufin duk abin da kuke yi, sa’ad da yake raye, ba aikin ido ba ne amma ƙauna ta gaske. Wannan yana nufin abu mai yawa a gare ni da kaina.
“Za mu tabbatar mun kammala dukkan ayyukan da ya bari a baya,” in ji shi.
Aiyedatiwa ya yi kira da a ci gaba da yin addu’o’i, inda ya ce, “Abin da za ku iya yi mana a yanzu shi ne ku ci gaba da yi mana addu’a Allah Ya ba mu baki daya karfin jure wannan rashi.