fidelitybank

Zan kai Buhari kotu idan yaci bashin dala miliyan 800 – Ndume

Date:

Dan Majalisar Dattijai mai wakiltar mazabar Borno ta Kudu, Sanata Mohammed Ali Ndume, ya yi barazanar kai gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari kotu idan ta karbo rancen dala miliyan 800.

A farkon watan Mayu ne shugaban ya aika wa majalisar dattawan ƙasar wata takarda da ke neman majalisar ta amince masa karɓo bashin kudin daga bankin duniya domin rage raɗaɗin da za a sha sanadin cire tallafin mai.

Hakan na zuwa ne bayan sanarwar da gwamnatin tarayya ta yi cikin watan Afirilu na bayar da tallafin dala miliyan 800 na bankin duniya ga ƴan Najeriya masu rauni su miliyan 50 ko gidaje miliyan 10.

Wannan batun dai ya janyo zazzafar muhawara kuma Sanata Ndume na cikin masu sukar matakin.

Dan majalisar ya ce ya kamata a ci bashi ne don a yi wa mutane abin da zai amfane su.

Dan majalisar ya ce kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba, saboda idan aka raba wa mutum miliyan 50 kudin abin da mutum daya zai samu ba zai wuci naira 7,200 bisa la’akari da canjin dala.

“Idan za a ci bashin a bai wa kananan hukumomi su yi ayyukan da al’umma za su ci moriyarsu to da sauki, amma ni ba na goyon bayan a ciwo bashi sannan a cinye.

Yadda aka zabi wadanda za su ci moriyar kudin da kuma cewa dukkan ‘yan Najeriya ne za su biya abu ne da ya sabawa kundin dokar Naajeriya” a cewar Sanata Ndume.

Har’ilayau, dan majalisar ya ce ba ya goyon bayan a ciwo bashi sannan wasu mutanen daban su cinye a bar gwamnati da biya.

Ya kuma kara da cewa ko da Shugaba Buhari ne ya saurari bayaninsa zai iya fada mishi ya je kotu kan batun.

Gwamnatin Najeriya dai ta ce za a rarraba tallafin ne don rage wa mutane wahalar da za su iya shiga idan aka cire tallafin mai.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp