Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, ya jaddada aniyarsa ta samar da shirye-shirye da za su kawo sauyi a Najeriya idan aka zabe shi.
Mista Obi, wanda ya taba zama gwamnan Anambra a wani lokaci, ya yi wa ‘yan jarida jawabi bayan ganawar sirri da Gwamna Okezie Ikpeazu na Abia, ranar Asabar, a kauyen Umuobiakwa.
Ya ce ziyarar na ci gaba da tuntubar sa da masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan.
Mista Obi ya kuma kara da cewa ziyarar ta zo daidai da manufofinsa na ziyartar shugabanni da masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan.
Ya kara da cewa hakan kuma ya yi daidai da kishinsa na yiwa kasa hidima a matsayinsa na shugaban kasar Najeriya.
A cewarsa, ba za a iya magana a kan shugabanci a yankin Kudu maso Gabas ba tare da neman Mista Ikpeazu ba, yana mai nuni da cewa ziyarar ta musamman ce domin sanar da gwamnan kan burinsa.