fidelitybank

Zan iya janyewa daga mukami na idan Tinubu ya bani umarni – Keyamo

Date:

Mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Tinubu-Shettima, Festus Keyamo, ya bada sharadi na janyewa daga yakin neman zaben jam’iyyar All Progressives Congress, APC, dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu.

Keyamo ya ce zai bar mukaminsa idan Tinubu ya nemi ya janye karar da ya shigar a gaban kotu kan Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP.

Keyamo ya ce, kamata ya yi a damke Atiku a gurfanar da shi a gaban kuliya bisa zarginsa da laifin karya dokar da’a, halasta kudaden haram, cin amana da kuma hada baki.

Keyamo yana maida martani ne kan wani faifan bidiyo da wani mai fallasa Michael Achimugu ya yi, wanda ya tuhumi Atiku.

Achimugu ya yi ikirarin cewa tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi amfani da ababan hawa na musamman wajen wawure kudade a lokacin da yake mulki a tsakanin shekarar 1999 zuwa 2007.

Sai dai Keyamo da ya bayyana a shirin gidan Talabijin na Channels, ‘Politics Today’ a ranar Talata, ya ce: “A cikin shari’ar da suka kalubalanci shugabana (Bola Tinubu), da suka kawo jabun takardu daga Amurka, na ce a garzaya kotu. Fito da cikakkar ƙirjinku ku tafi kotu. Har yau sun gudu.

“Zan tafi kotu. Idan kuma Asiwaju ya ce, ‘Festus, kana karkatar da kai daga yakin neman zabe na, ka yi mani kamfen.’ Zan ce ka dauki kamfen din saboda wannan yana da amfani ga kasa. Na dauke shi da kaina.”

legit nig. news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp